Yadda Za A San Yesu

Sa’anda ka koyi yadda zaka san Yesu, ka fara sabon tafiya mai ban mamaki zuwa ga shirin Allah ga rayuwarka. Romawa 3:23 ya fade shi haka: Gama dukanmu mun yi zunubi, kuma mun kasa ga daukakar Allah. Sanin Yesu shi ne amincewa kana bukatan shi, Gaskantawa da abinda yayi maka da karban kyautarsa mai ban mamaki. Yana tabbatar da cewa baza ka iya yin rayuwan nan da kanka ba, cewa kayi zunubi kuma kana bukatan mai ceto.

Kuma labari mai dadi game da sanin Yesu , game da samun ceto, shi ne kyakkyawan musanya da ke faruwa a wancan lokacin. Kana ba shi dukan munanan abubuwa na zunubi da ka yi, don haka kuma, Allah zai baka komai da ya tanada gareka. Ko ka sani ko baka sani ba tukunna, Shirin sa domin rayuwarka yana da ban mamaki, kuma wannan ne farkon taku ga wancan tafiyar.

“Saboda kaunar da Allah yayi wa duniya har ya bada makadaicin Dansa, domin duk wanda ya gaskata da shi kada ya hallaka, sai dai ya sami rai madawwami.” – YAHAYA 3:16

ADU’A

Romawa 10:9 yace idan mun bayyana Ubangiji Allahnmu da bakinmu, kuma mun gaskanta cewa Allah ya tashe Dansa Yesu daga matattu, zamu sami ceto. Idan Yesu yana kiran ka zuwa ga kadaitaccen zumunta da shi, kuma kana shirye domin ka bi shi cikin komai da kake yi, Furta wannan adu’an da karfi:

Yesu, Na san nayi zunubi kuma ina bukatan Mai Ceto. Na gaskanta cewa sa’anda ka je ga Giciye, Ka je can ne domina da dukan zunubai na. Na amince ka cece ni a yanzu haka. Na baka rayuwa na. Yau, na san na cetu kuma ka gafarta mani, ka taimakeni in gane me ake nufi da in yi rayuwa domin ka kowane rana. Amin.

Facebook icon Twitter icon Instagram icon Pinterest icon Google+ icon YouTube icon LinkedIn icon Contact icon